Jirgin Sojin Najeriya ya bace a Adamawa
Rundunar Sojojin Najeriya tace wani Jirgin Sojinta ya bace tsawon kwanaki biyu a arewa maso gabacin kasar inda Sojojin ke yaki da Mayakan Boko Haram. Sanarwar da Sojojin na Najeriya suka fitar tace jirgin mai suna Alpha Jet da matukansa guda biyu ya bar sansaninsu a garin Yola Jihar Adamawa da misalin karfe 10:45 na safe a ranar Juma’a amma tun lokacin ba a ji duriyarsa ba.
Wallafawa ranar:
Janar Chris Olukolade yace tun lokacin babu wani labari game da jirgin, amma suna fadada bincike domin gano inda jirgin ya bace.
Sai dai Olukolade bai bayyana cewa ko sun yi amfani da jirgin wajen yaki da mayakan Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu