Isa ga babban shafi
Najeriya-Kamaru

Sojojin Kamaru sun yi wa Boko Haram luguden wuta

Sojojin kasar Kamaru sun kai Mayakan boko Haram farmaki inda suka kashe mayaka da dama tare da tarwatsa daya daga cikin sansaninsu da ke iyaka da Najeriya. Wata Majiyar tsaro a Kamaru tace Sojojin sun kai farmakin ne a ranar Laraba.

Sojojin Kamaru  da ke yaki da Mayakan Boko Haram a arewacin kasar
Sojojin Kamaru da ke yaki da Mayakan Boko Haram a arewacin kasar Reuters
Talla

Wannan kuma na faruwa ne duka kwanaki biyu bayan Mayakan Boko Haram sun karbe ikon Gamboru-ngala da ke kusa da kan iyaka da Kamaru.

Majiyar tace Sojojin sun yi wa Mayakan ruwan wuta ne a wani sansaninsu da ke Gamboru kusa da Fotokol amma ba tare da bayyana adadin ‘yayan kungiyar ta Boko Haram ba da aka kashe.

Wani Jami’in ‘Yan sanda ta tabbatarwa Kamfanin Dillacin labaran Faransa da farmakin akan ‘Yan Boko Haram.

Wakilin RFI Hausa a arewacin Kamaru Ahmed Abba yace mutanen Gomburu da Fotokol da dama ne suka tsere zuwa cikin Kamaru.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.