Isa ga babban shafi
Kamaru

Kamaru ta kori wasu manyan hafsan Sojinta

Shugaban kasar Kamaru Paul Biya ya yi wa wasu manyan sojojin kasar Korar kare daga aiki saboda sakaci har ‘yan kungiyar Boko Haram suka fi karfinsu, har ta kai ga kashe mutane bakwai da sace uwargidan wani kusa a gwamnatin kasar.

Sojin Kamaru da ke yaki da mayakan Boko Haram a kan iyaka da Najeriya.
Sojin Kamaru da ke yaki da mayakan Boko Haram a kan iyaka da Najeriya. AFP PHOTO / REINNIER KAZE
Talla

A Ranar lahadi ne wasu ‘Yan bindiga da ake kyautata zaton Mayakan kungiyar Boko Haram ne na Najeriya suka kai hare hare a garin Kolofata da ke arewacin Kamaru inda suka aikata ta’asa.

‘Yan bindigar sun yi awon gaba da ‘Yan Sanda tare da kashe Sojoji guda hudu.

Ta kafar Radiyon kasar, Gwamnatin Kamaru ta bayar da sanarwar korar Kanal Youssa Gedeon Kwamandan Jandarma a arewa mai nisa da kuma abokin aikinsa Kanal Justice Ngonga.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.