Isa ga babban shafi
Nijar

Bukukuwan ranar hadin-kan kasa a Jamhuriyar Nijar

A Jamhuriyar Nijar, yau ana gudanar da bukin ranar hadin-kan kasar, ranar da ta samo asali daga yarjejeniyar zaman lafiya ta farko daka kulla tsakanin ‘yan tawaye da gwamnatin kasar a ranar 24 ga watan Afrilun shekarar 1995.

Mahamadou Issoufou, shugaban Jamhuriyar Nijar
Mahamadou Issoufou, shugaban Jamhuriyar Nijar France 24
Talla

An dai kulla yarjejeniyar a lokacin tsohon shugaban kasar marigayi Janar Ibrahim Ba’are Mainasara, wanda tare da shiga tsakanin wasu kasashe masu makotaka da Nijar da suka hada Aljeriya, Chadi, Burkina Faso da kuma Mali aka cimma jituwa da Azbinawa da ke fada da gwamnatin kasar.

Tun a wannan lokaci ne dai ake gudanar da bukukuwa domin kara hada kan al’ummar kasar baki daya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.