Isa ga babban shafi
Masar

Bom ya kashe babban Jami’in ‘Yan sanda a Masar

Jami’an tsaro a kasar Masar sun tabbatar da mutuwar wani Janar din ‘Yan Sanda sakamakon wani bom da aka dasa a motarsa a birnin al Kahira, wannan kuma shi ne karo na biyar da ake kai wa Manyan Jami'an ‘Yan sanda hare hare a babban birnin kasar.

Harin Bom da aka kai wa wani Janar din 'Yan sanda a Masar
Harin Bom da aka kai wa wani Janar din 'Yan sanda a Masar REUTERS/Al Youm Al Saabi Newspaper
Talla

Irin wannan harin ne aka kai wa Ahamed Zak wani babban kwamandan Jami’an tsaro da ke sahun gaba wajen karya magoya bayan hambararren shugaban kasa Mohammed Morsi.

Wata kungiyar Mayakan Jihadi mai suna Ajnad Misr ta fito tana ikirarin daukar alhakin hare haren da aka kai wa Manyan Jami’an tsaro tare da yin gargadin ci gaba da kai hare haren domin daukar fansa akan magoya bayan Morsi da aka kashe.

Amma akwai wata kungiyar Mayakan Jihadi ta Ansar Beit al-Magdis da ta yi ikirarin kai wasu hare haren kan ‘Yan sanda hadi da harin da aka kai a mashigin Sinai.

Tuni Gwamnatin Masar ta haramta ayyukan kungiyar 'Yan uwa Musulmi ta hambararren shugaban kasa Mohammed Morsi tare da jefa ta cikin jerin kungiyoyin 'Yan ta'adda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.