'Yan mata 234 ne suka rage hannun 'yan Boko Haram
Adadin dalibai matan da aka sace a garin Chibok na jihar Borno a Tarayyar Najeriya ya dada karuwa, inda yanzu haka ake cewa dalibai 234 aka yi garkuwa da su ba wai sama da 100 ba kamar yadda aka bayyana a baya.
Wallafawa ranar:
Sabon adadin ya bayyana ne yayin da gwamnan Jihar Kashim Shetima tare da Sanata Ali Ndume suka ziyarci garin na Chibok domin mika wasu daga cikin yaran da suka gudu daga hannun wadanda suka kama su.
Sanata Ali Ndume ya shaida wa gidan rediyo Faransa cewa sun zanta da iyayen yaran da suka bata, kuma sun tabbatar masa da cewa akwai ‘yan mata 234 da har yanzu ba su dawo ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu