Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya: Jonathan bai gayyaci Gwamnonin APC ba a taron tsaro

Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya gudanar da taron gaggawa kan kokarin magance matsalar tsaro ba tare da Gwamnonin Jam’iyar APC mai adawa ba. Gwamnan Jahar Adamawa Murtala Nyanko yace sun kauracewa taron ne saboda ba a gayyace su ba.

Wasu daga cikin Gwamnonin Arewacin Najeriya
Wasu daga cikin Gwamnonin Arewacin Najeriya www.bellanaija.com
Talla

Taron wanda ya kunshi manyan Jami’an tsaro da Gwamnonin Jahohin kasar an gudanar da shi ne ba tare an bayyana matsayar da aka cim ma ba akan yadda za’a magance matsalar tsaron da ke addabar yankin arewaci.

01:30

Rahoton Kabir Yusuf daga Abuja

Kabir Yusuf

Wasu kafofin yada labarai a Najeriya sun ruwaito wani babban na hannun damar shugaba Jonathan yana tabbatar da cewea gangan gwamnatin PDP ta ki gayyatar Gwamnonin na APC.

Gwamnan Jahar Adamawa Murtala Nyako ya shaidawa RFI Hausa cewa bayan sun hallara zuwa Abuja daga baya aka shaida masu cewa an dage taron.

Jam’iyyar APC ce dai ke mulki a dukkanin Jahohi uku a yankin arewa maso gabaci da ke cikin dokar ta-baci da gwamnatin Jonathan ta kafa saboda kazancewar matsalar tsaro amma an gudanar da taron ne ba tare da wani daga cikinsu ba saboda wasu dalilai na siyasa.

01:14

Gwamnan Jahar Adamawa Murtala Nyako

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.