Najeriya -
Wallafa labari : Laraba 19 Satumba 2012 -
Bugawa ta karshe : Laraba 19 Satumba 2012
‘Yan bindiga sun harbe kwamishinan Shari’a a Najeriya

Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan
‘Yan bindiga a Maiduguri, sun hallaka kwamishinan shari’ar Jihar Barno, Zanna Malam Gana, a kauyan sa dake Bama. Wannan na zuwa ne kwana guda bayan harin da aka kaiwa Tsohon shugaban gandirebobin Nigeria, Ibrahim Jarma a Azare, inda aka raunana shi, kana kuma aka hallaka dogarin sa.
“Mun samu bayanan rasuwar kwamishinan shari’a Zannah Malam Gana, wasu mutane dauke da bindiga ne su ka harbe shi a gidansa da misalin 8:45 na yamma a daren jiya” inji wani Jami’in gwamnati.
Shi kuwa Shugaban gandirobobin, an kashe ne a Jihar Bauchi a yayin da ya ke barin masallaci zuwa gidansa.
KAN MAUDU'I GUDA

Delicious
Digg
Facebook
Twitter
Yahoo!
Technorati








Ra'ayoyi
Bada ra'ayi kan wannan magana