Masar - 
Wallafa labari : Alhamis 02 Feberairu 2012 - Bugawa ta karshe : Alhamis 02 Feberairu 2012

Mutane 74 sun mutu a filin wasan kwallon kafa a Masar

Filin wasan kwallon kafar birnin Port said inda rikici ya barke tsakanin magoya bayan kungiyoyin kwallon kafa a kasar Masar
Filin wasan kwallon kafar birnin Port said inda rikici ya barke tsakanin magoya bayan kungiyoyin kwallon kafa a kasar Masar
REUTERS/Stringer

Daga Awwal Ahmad Janyau

A Kasar Masar, Akalla mutane 74 suka mutu wasunsu kuma da dama suka jikkata sanadiyar wani rikici daya barke a filin wasan kwallon kafa tsakanin abokan hammaya a birnin Port Said. Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA tace wannan ranar bakin ciki ga kwallon kafa.

wannan rikicin shi ne irinsa na farko a tarihin kwallon kafa, kuma rikicin ya barke ne bayan fura usul ta karshe da alkalin wasa ya yi inda kungiyar Al Masri ta doke Al Ahly ta Al kahira ci 3-1.

A filin wasan dai an yi musayar duwatsu ne da farfasa kwalabe tsakanin magoya bayan kungiyoyin kwallon kafar guda biyu.

Yanzu haka dai a shafin Internet akwai hutunan dimbim mutane da rikicin ya rutsa dasu jina jina.

Jam’iyyar Musulunci ta Brotherhood ta zargi magoya bayan hambararren shugaban kasar Hosni Mubarak da kitsa rikicin.

Sai dai a yau ne majalisar kasar karkashin jagorancin Fira Minista Kamal Ganzuri, zasu gana domin tattauna wannan rikicin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 74.

 

tags: Kwallon Kafa - Masar - Wasanni
KAN MAUDU'I GUDA
Ra'ayoyi
Bada ra'ayi kan wannan magana
The content of this field is kept private and will not be shown publicly.
To prevent automated spam submissions leave this field empty.
CAPTCHA
This question is for testing whether you are a human visitor and to prevent automated spam submissions.
Image CAPTCHA
Enter the characters (without spaces) shown in the image.
Close