Afrika

Syndicate contentAfrika
Wani manomi a yankin kasar Chadi
16/05/2012 - MDD-Afrika

Sai an Magance Yunwa kafin a samu ci gaba a Afrika, Inji MDD

Hukumar Ci gaba ta Majalisar Dinkin Duniya, tace dole sai kasashen Afrika sun magance matsalar yunwa da ke addabar kasashe 27 a nahiyar kafin kasancewa matsayin Yankin da ya samu ci gaba.

Gungun mata da Amaren da aka daurawa aure a Kano
16/05/2012 - Najeriya

Hisbah ta daura auren Zawarawa 100 a Kano

Hukumar Hisbah a Jihar Kano, ta daura wa Zawarawa 100 aure cikin 1,000 da aka shirya yi, dan magance mace macen aure a Jahar.

kamfanin Areva, mallakar kasar Faransa, da ke hako ma’adinin uranium a Yankin Arlit a Jamhuriyyar Nijar
15/05/2012 - Nijar-Faransa

Wata kungiyar Farin kaya ta nemi kamfani Areva ya biya ‘Yan Nijar diyya

Wata Kungiyar fararen hula a Jamhuriyar Nijar, ta bukaci kamfanin Areva, mallakar kasar Faransa, da ke hako ma’adinin uranium a kasar, biyan kudaden Diyya ga ‘Yan Nijar dai dai da yadda Kamfanin ke biyan Faransawan da suka mutu.

Taswirar kasar Guinea Bissau da kasashen da ke makwabtaka da kasar
15/05/2012 - ECOWAS-Guinea Bissau-Najeriya

Najeriya zata tura dakarunta zuwa Guinea Bissau

Gwamnatin Najeriya tace zata girke dakarunta a kasar Guinea Bissau don taimakawa kasar komawa ga mulkin fararen hula, kamar yadda kungiyar ECOWAS ta bukata.

Caesar Acellam
14/05/2012 - Uganda

An cafke wani jagoran ‘Yan tawayen LRA a Uganda

Hukumomin Kasar Uganda sun ce, sun yi nasarar kama Caeser Acellam wani babban kusa a kungiyar ‘Yan Tawayen Lords Resistence Army, da ke karkashin Joseph Kony. Kakakin rundunar sojin Uganda, Lt Col Felix Kulayigye, yace Acellam ne jami’I na hudu a kungiyar ‘Yan Tawayen, bayan Joseph Kony, da Dominic Ongwen da Okot Odhiambo.

Dakarun Sudan a yankin Heglig daya daga cikin yankunan da ake rikici tsakanin Sudan da Sudan ta Kudu
14/05/2012 - MDD-Sudan

Ban Ki-moon ya bukaci Sudan janye Dakarunta daga Abyei

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki Moon, ya bukaci Sudan ta janye dakarun ta daga Yankin Abyei da ake takaddama akai. Ban wanda yake jawabi bayan ficewar dakarun Sudan ta kudu, ya bukaci kasashen biyu su mutunta yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya.

Taron shugabannin kasashen Kungiyar ECOWAS bayan kammala taro a Dakar kasar Senegal game da rikicin siyasar Mali da Guine Bissau
14/05/2012 - ECOWAS-Mali-Guinea Bissau

Hafsoshin Sojin ECOWAS zasu gana a Najeriya game da Guinea Bissau da Mali

A Yau Litinin ne Manyan Hafsoshin sojin kasashen Afrika ta Yamma zasu gudanar da wani taro a Abuja babban birnin Najeriya, don nazarin hanyoyin da zasu bi wajen girke dakaru a kasar Guinea Bissau da Mali.

11/05/2012 - Senegal

An buda bikin nuna al'adun sana'oin hannu na Afrika a kasar Senegal (Dak’Art)

A yau juma’a shugaban kasar Senegal Macky Sally a buda soma wani gawurtacen bikin al’adu na kirkire kirkiren ayukan hanu na nahiyar Afrika a birnin Dakar babban birnin kasar ta Senegal (Dak’Art).

Plus de 21 millions d'Algériens se rendent aux urnes ce jeudi 10 mai pour élire leurs députés.
11/05/2012 - Algeriya

Jam,iyar RCD a kasar Aljeriya ta ce kashi 18% na masu zabe ne suka halarci zaben jiya alhamis

Jamiyar RCD da ta kauracewa zaben yan majalisar dokokin da aka gudanar a jiya alhamis a kasar Aljeriya, ta kalubalanci sakamakon da gwamnatin kasar ta bayar, kan yawan jama’ar da suka halarci zaben na kashi 42,9%, inda ta ce sakamakon bai wuce kashi 18% ba, kamar yadda shugaban jami’iyar Mohcin Bellabas ya sanar.

10/05/2012 - Sharhin Jaridu

Sharhin jaridun duniya

Jaridar Punch: (Najeriya)

Gwanatin jihar Legas jiya tace a shirye ta ke ta koma kan teburin tattaunawa, da likitocin da ta kora a shekaran jiya.

Shugaban Cote d'IVoire Alassane Ouattara kuma shugaban ECOWAS a lokacin da yake ganawa da Goodluck Jonathan na Najeriya a filin saukar jirgi na Felix Houphouet Boigny a Abidjan
10/05/2012 - ECOWAS-Guinea Bissau-Najeriya

ECOWAS zata tura Tawaga zuwa G/Bissau, inji Goodluck

A wata ziyara da kai kasar Cote d’Ivoire, Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan, yace kungiyar kasashen Afrika ta Yamma, ECOWAS, zata tura wata tawaga zuwa kasar Guinea Bissau don tattaunawa da sojojin kasar, domin ganin sun mayar da kundin tsarin mulki.

Wasu mata suna tafiya kusa da hutunan 'Yan siyasa da aka lika a bangon a birnin Algiers.
10/05/2012 - Algeria

Zaben ‘Yan Majalisa a Algeria

Al’ummar Algeria sun fara kada kuri’arsu a zaben farko na ‘Yan Majalisu tun fara zanga-zangar kasashen Larabawa, inda Jam’iyyar Mai mulki da Jam’iyyar ‘yan uwa musulmi ke fatar samun rinjayen kujeru tsakanin Jam’iyyu 44 da suka shiga takarar zaben ‘Yan Majalisa 462.

Garken Rakuma suna sha ruwa a gabar Tabkin Chadi da ke kewaye da tsaunuka
09/05/2012 - Nijar-Najeriya-Chadi

Kasashen raya tabkin Chadi zasu samar da dakarun hadin gwiwa don yaki da Ta’addanci

Manyan Jami’an tsaron kasashen da ke raya tafkin Chadi, sun gudanar da taro a Jamhuriyar Nijar, don nazarin hanyoyin da zasu dakile safarar makamai da kuma ayyukan ta’adanci domin samun ci gaban kasashensu.

Jerin Mata masu shayarwa a Nijar suna jiran Likita
09/05/2012 - Nijar-Save the Children

Nijar ta yi watsi da rahoton Save The Children akan Mata

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta yi watsi da rahotan kungiyar agaji ta Save the Children, wanda yace mata na fama da tsananin wahala wajen haihuwa da kuma renon kananan yara, abinda ya sa kasar ta zama ta karshe a mizanin kasashen duniya 165.

'Yan tawayen Libya rike da muggan makamai a lokacin yaki da dakarun Marigayi Gaddafi
09/05/2012 - Libya

An yi musayar Albarussai tsakanin ‘Yan bindiga da jami’an tsaron Libya

A kasar Libya mutane da dama sun samu rauni tare da samun mutuwar mutum daya sakamakon musayar wuta da aka yi tsakanin Jami’an tsaro da ‘Yan bindiga dwadanda suka yi zanga zanga a Hedikwatar Gwamnati a Birnin Tripoli.

Likitocin Najeriya a Jahar Legas lokacin da suke maci domin neman biyansu kudaden Albashi
08/05/2012 - Najeriya

Gwamnatin Jahar Legas a Najeriya ta kori Likitoci 788

Hukumomin Jahar Legas a Najeriya sun tabbatar da sallamar Likitoci 788 wadanda ke yajin aiki tsawon makwanni uku. Gwamnatin Jahar Legas tace yajin aikin Likitocin ya sabawa doka.

'Yan Acaba a Najeriya
07/05/2012 - Najeriya

Gwamnatin Flato a Najeriya ta haramta yin Acaba

Gwamnatin Jahar Flato a Najeriya ta sanar da haramta yin Acaba da babura a birnin Jos da kewaye, saboda yunkurin dakile ayyukan laifi da ake da baburan, kamar yadda ta sanar bayan taron Majalisar ...

Masu gabatar da kara  Brenda J. Hollis da, Nicholas Koumjian da Mohammed Bangura a sauraren karar Charles Taylor
04/05/2012 - Liberia-Saliyo

Mai gabatar da kara ya nemi a yanke wa Taylor hukuncin shekaru 80 a gidan yari

Babban mai gabatar da kara a shari’ar Charles Taylor tsohon shugaban kasar Liberia, ya nemi a daure tsohon shugaban shekaru 80 a gidan yari bayan kama shi da laifin aikata laifukan yaki a Saliyo.

Janar Bosco Ntaganda,
04/05/2012 - Jamhuriyyar Congo

Dakarun Congo sun ce sun isa mafakar Ntaganda da ake nema ruwa a jallo

Dakarun Sojan kasar Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo, sun ce sun isa, zuwa maboyar gudajjen janar din sojan kasar Jean Bosco Ntaganda, da ake zargi da haddasa tashin hankalin da ya yi sanadiyyar dubun dubatan mutane rasa gidajensu.

Le corps du guide libyen, Mouammar Kadhafi  le 21 octobre 2011, à Misratra.
03/05/2012 - Libya-kotun duniya

yar tsohon shugaban kasar Libiya Marigayi Ma'amar Kaddafi ta nemi a yi binciken yadda aka kashe mata uba

‘Yar marigayi Moammar Gaddafi na kasar Libya, Aisha Gaddafi ta nanata bukatar ganin Hukumomin fadin duniya sun tallafa mata tilasta binciken yadda aka kashe mahaifinta da wani dan-uwanta ...

Close