Shugaban kungiyar Boko Haram Imam Abubakar shakau ya sake aiko da wani sako ta You Tube a Intanet inda ya yi ikirarin daukar alhakin kai harin Kano domin mayar da martanin muzgunawa mambobin kungiyarsu.
A Makon jiya ne wata kungiyar Musulmi a birnin Kano ta ziyarci Kiristocin da ke birnin, inda ta yi alkawarin samar musu da tsaro daga hare haren da ake samu a wasu sassan Arewacin Najeriya. Wannan mataki ya bude wani sabon babi a kasar, inda aka samu irin wannan fahimta a Abuja da Jahar Niger. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Arch Bishop, Ignatius Kaigama game da wannan fahimta da ake samu tsakanin bangarorin biyu.