Tsohon kwamandan Serbia, Janar Ratko Mladic, ya gurfana a gaban kotun Duniya a birnin Hague domin fuskantar zargi 11 na laifukan yaki da kisan kare dangi da keta hakkin bil’adama a yakin Bosnia a shekarar 1992-95.
A hirar shi da Rediyo Faransa, Mai Martaba Sarkin Gwandu mai Murabus, Manjo Mustapha Haruna Jokolo kuma Tsohon Dogarin Janar Muhammadu Buhari, yace babu wani ci gaba da shugabannin Arewa suka tsinanawa yankin bayan kwashe shekaru ‘Yan arewa na mulki a Najeriya. Jokolo yace ci gaban da gwamnatin su Sardauna suka samar a Arewa yanzu sai dai Tarihi.