Kasar Amurka da Birtaniya sun janye jakadunsu daga kasar Syria saboda fargabar tsaro da rashin amincewa da yadda ake ci gaba da murkushe masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Bashar al Assad.
A yau Litinin ne Al’ummar musulmi ke gudanar da bukin haihuwar Annabi Muhammad SAW musamman mabiya akidar Darika, bukin da ya sabawa ‘Yan sunni. Sai dai sheikh Dahiru Bauchi a Najeriya a hirar shi da Rediyon Faransa yace a ka’idar musulunci akwai wata rana da ake kebewa ta murna domin godewa Allah ni’imarsa saboda samun Al Kur’ani mai girma.